x

Kwalejin Kimiyya Da Fasaha Da Jami’ar Aliko Dangote Sun Kulla Yarjejeniyar Alakar Karatu.

JABIRU HASSAN, Daga Kano.

A Tamar Litinin din data gabata, watau 29 ga watan Yuli, shekara ta 2024 Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic tare da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote dake Garin Wudil suka rattaba hannu akan jarjejeniyar kulla alakar gabatar da karatun Postgraduate Diploma a bangarorin Kimiyya, Fasaha da Kuma Kere-kere.

A jawabin da ya gabatar a yayin rattaba hannun, Shugaban Jami’ar Fasaha ta Wudil, Farfesa Musa Tukur Yakasai Ya bayyana matukar Jin dadinsa ga wannan hobbasa da Kwaleji Kimiyya ta Kano ta bijiro da shi wajen ganin ta cimma mafarkin da ta dade tana yi.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka zata samar da matukar cigaba wajen bunkasa harkokin Kere-kere a fadin Jihar Kano dama Kasa baki daya.

Farfesa Yakasai Ya jaddada cewa a yanzu Jami’arsu ta sahalewa Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic ta fara gabatar da karatun Postgraduate Diploma a fannoni guda 9, tare da tabbatar da cewa nan gaba kadan za’a Kara shigo da wasu sababbin kwasa-kwasan a wannan hadaka.

Ya kuma yabawa Shugaban Kwalejin, Dr. Abubakar Umar Farouq, FCA wajen jajircewarsa don ganin an cimma wannan nasara.

A nasa jawabin, Shugaban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, Dr. Abubakar Umar Farouq Ya bayyana matukar Jin dadinsa tare da mika godiya ga Allah da Ya nuna masa wannan rana ta saka hannun akan wannan yarjejeniya.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka tsakanin makarantun Kimiyya da Fasaha mallakin Jihar Kano guda biyu zai matukar taimakawa kokarin da Gwamnatin Jihar Kano, karkashin Jagoranci Alhaji Abba Kabir Yusuf take wajen ganin ta bunkasa ilimi, musammam na bangaren Kimiyya da Fasaha.

Dr. Farouq Ya jaddada cewa wannan hadaka zata baiwa dumbin matasa da masu sha’awar cigaba da karatu damar cimma burikansu ba tare da wahala ba.

A karshe Ya godewa Shugaban Jami’ar ta Wudil gami da masu taimaka masa wajen ganin an cimma wannan nasara, tare da tabbatar da cewa Kwalejin Fasaha ta Kano za tayi duk Maiyiwuwa wajen ganin komai Ya tafi akan tsari.

Hot this week

Editors Urge Government To Create Safe, Enabling Environment For Journalists

· Ask security agents to find missing Vanguard journalistAs...

EXCLUSIVE: Buhari orders probe of Isa Funtua, AMCON over keystone and Etisalat

Following the controversy generated by the leading opposition party,...

6 Signs your boyfriend thinks you are ugly -Take note of No. 2

They say there are three kinds of people; the...

2023: South-East, Middle Belt Forum Endorses Peter Obi

The South-East and Middle Belt Forum has endorsed the...

Dr. Uduak Silas Obot Laid to Rest in His Country Home

Amgbare Ekaunkumo, YenagoaThe remains of Dr. Uduak Silas Obot,...

Bayelsa Governor Lauds Security Agencies for Synergy

Amgbare Ekaunkumo, YenagoaBayelsa State Governor, Senator Douye Diri has...

Bayelsa Cult Attack Claims Two Lives

Amgbare Ekaunkumo, YenagoaTwo Niger Delta University graduates were brutally...

B’Haram: Zulum approves 35 patrol vehicles, motorcycles for Borno community

By Achadu Gabriel, KadunaBorno State Governor, Babagana Umara Zulum,...

Adulterated soya beans oil producing factory discover in Kaduna

By Achadu Gabriel, kadunaApparently owing to severity of hardship...

Judge Faces Compulsory Retirement for Misconduct in Kogi

By Noah Ocheni, LokojaAn area court Judge, Alemeru Adekunle...

Wike Hints, Tinubu’s Behind ICC Facelift To World Class Facility

By Joyce Remi-BabayejuThe FCT Minister Barr. Nysome Wike has...
spot_img

Related Articles

Popular Categories

spot_imgspot_img