x

Kwalejin Kimiyya Da Fasaha Da Jami’ar Aliko Dangote Sun Kulla Yarjejeniyar Alakar Karatu.

JABIRU HASSAN, Daga Kano.

A Tamar Litinin din data gabata, watau 29 ga watan Yuli, shekara ta 2024 Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic tare da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote dake Garin Wudil suka rattaba hannu akan jarjejeniyar kulla alakar gabatar da karatun Postgraduate Diploma a bangarorin Kimiyya, Fasaha da Kuma Kere-kere.

A jawabin da ya gabatar a yayin rattaba hannun, Shugaban Jami’ar Fasaha ta Wudil, Farfesa Musa Tukur Yakasai Ya bayyana matukar Jin dadinsa ga wannan hobbasa da Kwaleji Kimiyya ta Kano ta bijiro da shi wajen ganin ta cimma mafarkin da ta dade tana yi.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka zata samar da matukar cigaba wajen bunkasa harkokin Kere-kere a fadin Jihar Kano dama Kasa baki daya.

Farfesa Yakasai Ya jaddada cewa a yanzu Jami’arsu ta sahalewa Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic ta fara gabatar da karatun Postgraduate Diploma a fannoni guda 9, tare da tabbatar da cewa nan gaba kadan za’a Kara shigo da wasu sababbin kwasa-kwasan a wannan hadaka.

Ya kuma yabawa Shugaban Kwalejin, Dr. Abubakar Umar Farouq, FCA wajen jajircewarsa don ganin an cimma wannan nasara.

A nasa jawabin, Shugaban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, Dr. Abubakar Umar Farouq Ya bayyana matukar Jin dadinsa tare da mika godiya ga Allah da Ya nuna masa wannan rana ta saka hannun akan wannan yarjejeniya.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka tsakanin makarantun Kimiyya da Fasaha mallakin Jihar Kano guda biyu zai matukar taimakawa kokarin da Gwamnatin Jihar Kano, karkashin Jagoranci Alhaji Abba Kabir Yusuf take wajen ganin ta bunkasa ilimi, musammam na bangaren Kimiyya da Fasaha.

Dr. Farouq Ya jaddada cewa wannan hadaka zata baiwa dumbin matasa da masu sha’awar cigaba da karatu damar cimma burikansu ba tare da wahala ba.

A karshe Ya godewa Shugaban Jami’ar ta Wudil gami da masu taimaka masa wajen ganin an cimma wannan nasara, tare da tabbatar da cewa Kwalejin Fasaha ta Kano za tayi duk Maiyiwuwa wajen ganin komai Ya tafi akan tsari.

Hot this week

Reps Urge FG to Harmonise Poverty Reduction Programmes

The House of Representatives has urged the Federal Government...

MOT!ON Raises Concerns Over Electoral Act 2022 Review, Questions NASS Intentions

The Movement for the Transformation of Nigeria (MOT!ON) has...

Ibeno stakeholders Dismantle Ekid Claims over Stubb Creek, Affirm Constitutional Ownership

By Ogenyi Ogenyi,Uyo.The Ibeno people have reaffirmed their historical,...

CACOL Calls for Release of Protesters Arrested Over Demolition Protests in Lagos

The Centre for Anti-Corruption and Open Leadership (CACOL) has...

National Youth Alliance Inaugurates State Chairmen, Launches Digital Portal

The National Youth Alliance (NYA) has inaugurated chairmen for...

Airports, Drug Syndicates, and Nigeria’s Global Reputation

By Tahir WaliNigeria’s airports are more than transit points;...

Kogi Govt Says Cash-Back Promotion Policy Boosts Workers’ Welfare

By Noah Ocheni, LokojaThe Kogi State Government says its...

Bayelsa Lays Late Deputy Governor to Rest as Tinubu, Jonathan Pay Tributes

By Amgbare Ekaunkumo, YenagoaBayelsa State on Saturday laid to...

Humanitarian:President Shettima Commissions Tudun Biri Resettlement Site in Kaduna

By Joyce Remi-BabayejuThe Vice President, Senator Kashim Shettima, has...

Army kills ISWAP commander, foils attacks in Borno

Troops of the Joint Task Force (North East), Operation...

Premier League Clubs Step Up Activity as January Transfer Window Nears Close

Premier League clubs intensified squad reshaping during the January...

March 31 Deadline: Oyedele Urges Nigerians to File Annual Tax Returns

Chairman of the Presidential Committee on Fiscal Policy and...

Crusade Dispute Puts CAN, PFN Under Spotlight

Allegations of interference and partiality have unsettled Nigeria’s major...

Related Articles

Popular Categories

spot_imgspot_img