x

Kwalejin Kimiyya Da Fasaha Da Jami’ar Aliko Dangote Sun Kulla Yarjejeniyar Alakar Karatu.

JABIRU HASSAN, Daga Kano.

A Tamar Litinin din data gabata, watau 29 ga watan Yuli, shekara ta 2024 Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic tare da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote dake Garin Wudil suka rattaba hannu akan jarjejeniyar kulla alakar gabatar da karatun Postgraduate Diploma a bangarorin Kimiyya, Fasaha da Kuma Kere-kere.

A jawabin da ya gabatar a yayin rattaba hannun, Shugaban Jami’ar Fasaha ta Wudil, Farfesa Musa Tukur Yakasai Ya bayyana matukar Jin dadinsa ga wannan hobbasa da Kwaleji Kimiyya ta Kano ta bijiro da shi wajen ganin ta cimma mafarkin da ta dade tana yi.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka zata samar da matukar cigaba wajen bunkasa harkokin Kere-kere a fadin Jihar Kano dama Kasa baki daya.

Farfesa Yakasai Ya jaddada cewa a yanzu Jami’arsu ta sahalewa Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic ta fara gabatar da karatun Postgraduate Diploma a fannoni guda 9, tare da tabbatar da cewa nan gaba kadan za’a Kara shigo da wasu sababbin kwasa-kwasan a wannan hadaka.

Ya kuma yabawa Shugaban Kwalejin, Dr. Abubakar Umar Farouq, FCA wajen jajircewarsa don ganin an cimma wannan nasara.

A nasa jawabin, Shugaban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, Dr. Abubakar Umar Farouq Ya bayyana matukar Jin dadinsa tare da mika godiya ga Allah da Ya nuna masa wannan rana ta saka hannun akan wannan yarjejeniya.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka tsakanin makarantun Kimiyya da Fasaha mallakin Jihar Kano guda biyu zai matukar taimakawa kokarin da Gwamnatin Jihar Kano, karkashin Jagoranci Alhaji Abba Kabir Yusuf take wajen ganin ta bunkasa ilimi, musammam na bangaren Kimiyya da Fasaha.

Dr. Farouq Ya jaddada cewa wannan hadaka zata baiwa dumbin matasa da masu sha’awar cigaba da karatu damar cimma burikansu ba tare da wahala ba.

A karshe Ya godewa Shugaban Jami’ar ta Wudil gami da masu taimaka masa wajen ganin an cimma wannan nasara, tare da tabbatar da cewa Kwalejin Fasaha ta Kano za tayi duk Maiyiwuwa wajen ganin komai Ya tafi akan tsari.

Hot this week

Julius Berger has done a very beautiful job on Bodo-Bonny Road – Tinubu

By Francis WilfredPresident Bola Ahmed Tinubu has hailed leading...

Bandits Attack Kogi Communities, Kill Residents and Abduct Others in Mopamuro

By Noah Ocheni, LokojaBandits attacked two communities in Mopamuro...

Maikaya Praises Balarabe’s Developmental Legacy in Toto LGA Ahead of 2027 Elections

From Abel Zwanke, LafiaAhead of the 2027 general elections,...

Landlord Moves to Evict 2Baba and Natasha Over Alleged...

Northern Group Calls for Youth and Women Development, Honours Hajiya Farida Jauro

From Abel Zwanke, LafiaA Northern advocacy group, the Coalition...

Maikaya Praises Balarabe’s Developmental Legacy in Toto LGA Ahead of 2027 Elections

From Abel Zwanke, LafiaAhead of the 2027 general elections,...

Anioma, Igbanke Communities Endorse Anioma State Creation, Seek Zoning to South-East

  By Anne AzukaA coalition of Anioma people in Delta...

Delta Government Backs Anioma State Creation, Insists on Constitutional Due Process

 By Anne AzukaThe Delta State Government has declared that...

Kano State Government Celebrates AIT at 29, Hails Role in Nation-Building

  By Jabiru HassanThe Kano State Government has congratulated African...

Related Articles

Popular Categories

spot_imgspot_img