x

Kwalejin Kimiyya Da Fasaha Da Jami’ar Aliko Dangote Sun Kulla Yarjejeniyar Alakar Karatu.

JABIRU HASSAN, Daga Kano.

A Tamar Litinin din data gabata, watau 29 ga watan Yuli, shekara ta 2024 Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic tare da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote dake Garin Wudil suka rattaba hannu akan jarjejeniyar kulla alakar gabatar da karatun Postgraduate Diploma a bangarorin Kimiyya, Fasaha da Kuma Kere-kere.

A jawabin da ya gabatar a yayin rattaba hannun, Shugaban Jami’ar Fasaha ta Wudil, Farfesa Musa Tukur Yakasai Ya bayyana matukar Jin dadinsa ga wannan hobbasa da Kwaleji Kimiyya ta Kano ta bijiro da shi wajen ganin ta cimma mafarkin da ta dade tana yi.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka zata samar da matukar cigaba wajen bunkasa harkokin Kere-kere a fadin Jihar Kano dama Kasa baki daya.

Farfesa Yakasai Ya jaddada cewa a yanzu Jami’arsu ta sahalewa Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic ta fara gabatar da karatun Postgraduate Diploma a fannoni guda 9, tare da tabbatar da cewa nan gaba kadan za’a Kara shigo da wasu sababbin kwasa-kwasan a wannan hadaka.

Ya kuma yabawa Shugaban Kwalejin, Dr. Abubakar Umar Farouq, FCA wajen jajircewarsa don ganin an cimma wannan nasara.

A nasa jawabin, Shugaban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, Dr. Abubakar Umar Farouq Ya bayyana matukar Jin dadinsa tare da mika godiya ga Allah da Ya nuna masa wannan rana ta saka hannun akan wannan yarjejeniya.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka tsakanin makarantun Kimiyya da Fasaha mallakin Jihar Kano guda biyu zai matukar taimakawa kokarin da Gwamnatin Jihar Kano, karkashin Jagoranci Alhaji Abba Kabir Yusuf take wajen ganin ta bunkasa ilimi, musammam na bangaren Kimiyya da Fasaha.

Dr. Farouq Ya jaddada cewa wannan hadaka zata baiwa dumbin matasa da masu sha’awar cigaba da karatu damar cimma burikansu ba tare da wahala ba.

A karshe Ya godewa Shugaban Jami’ar ta Wudil gami da masu taimaka masa wajen ganin an cimma wannan nasara, tare da tabbatar da cewa Kwalejin Fasaha ta Kano za tayi duk Maiyiwuwa wajen ganin komai Ya tafi akan tsari.

Hot this week

APC National Chairman Nentawe Launches 14-Day Free Medical Outreach in Plateau

**By Israel Adamu, Jos**The National Chairman of the All...

Arsenal Hand Goalkeeper David Raya Improved Contract

Arsenal have rewarded Spanish goalkeeper David Raya with an...

Senator Lalong Chairs UNIJOS Alumni Lecture, Calls for Safeguards in Justice Delivery in Digital Age

Senator Simon Bako Lalong, representing Plateau South Senatorial District...

20 Dead, Several Missing in Fresh Boat Mishap in Kogi

By Noah Ocheni, LokojaAt least 20 people have been...

Anambra Community to Bury Traditional Ruler October 9

The Oko community in Orumba North Local Government Area...

A’Ibom Police receive 255 new Recruits

By Ogenyi Ogenyi,UyoAkwa Ibom Commissioner of Police, Baba...

Army begins probe into murder of officer by wife in A’ibom

By Ogenyi Ogenyi, UyoThe Nigerian Army, 2 Brigade, Uyo...

Gov Mutfwang’s Re-Election, Most Noble Ambition for Plateau – Commissioner

By Israel Adamu, JosThe Commissioner for Local Government and...

ITF Celebrates 54th Anniversary, Pledges More Training for Artisans

By Israel Adamu, JosThe Industrial Training Fund (ITF), Nigeria’s...

A’ibom shrine crisis; NGO seeks truce, appeals for discretion

By Ogenyi Ogenyi,UyoA Non Governmental Organisation, Open Forum for...

APC National Chairman, Prof. Nentawe, Empowers Traders with ₦50 Million Cash

By Israel Adamu, JosThe National Chairman of the All...

Related Articles

Popular Categories

spot_imgspot_img