x

Kwalejin Kimiyya Da Fasaha Da Jami’ar Aliko Dangote Sun Kulla Yarjejeniyar Alakar Karatu.

JABIRU HASSAN, Daga Kano.

A Tamar Litinin din data gabata, watau 29 ga watan Yuli, shekara ta 2024 Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic tare da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote dake Garin Wudil suka rattaba hannu akan jarjejeniyar kulla alakar gabatar da karatun Postgraduate Diploma a bangarorin Kimiyya, Fasaha da Kuma Kere-kere.

A jawabin da ya gabatar a yayin rattaba hannun, Shugaban Jami’ar Fasaha ta Wudil, Farfesa Musa Tukur Yakasai Ya bayyana matukar Jin dadinsa ga wannan hobbasa da Kwaleji Kimiyya ta Kano ta bijiro da shi wajen ganin ta cimma mafarkin da ta dade tana yi.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka zata samar da matukar cigaba wajen bunkasa harkokin Kere-kere a fadin Jihar Kano dama Kasa baki daya.

Farfesa Yakasai Ya jaddada cewa a yanzu Jami’arsu ta sahalewa Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic ta fara gabatar da karatun Postgraduate Diploma a fannoni guda 9, tare da tabbatar da cewa nan gaba kadan za’a Kara shigo da wasu sababbin kwasa-kwasan a wannan hadaka.

Ya kuma yabawa Shugaban Kwalejin, Dr. Abubakar Umar Farouq, FCA wajen jajircewarsa don ganin an cimma wannan nasara.

A nasa jawabin, Shugaban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, Dr. Abubakar Umar Farouq Ya bayyana matukar Jin dadinsa tare da mika godiya ga Allah da Ya nuna masa wannan rana ta saka hannun akan wannan yarjejeniya.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka tsakanin makarantun Kimiyya da Fasaha mallakin Jihar Kano guda biyu zai matukar taimakawa kokarin da Gwamnatin Jihar Kano, karkashin Jagoranci Alhaji Abba Kabir Yusuf take wajen ganin ta bunkasa ilimi, musammam na bangaren Kimiyya da Fasaha.

Dr. Farouq Ya jaddada cewa wannan hadaka zata baiwa dumbin matasa da masu sha’awar cigaba da karatu damar cimma burikansu ba tare da wahala ba.

A karshe Ya godewa Shugaban Jami’ar ta Wudil gami da masu taimaka masa wajen ganin an cimma wannan nasara, tare da tabbatar da cewa Kwalejin Fasaha ta Kano za tayi duk Maiyiwuwa wajen ganin komai Ya tafi akan tsari.

Hot this week

Editors Urge Government To Create Safe, Enabling Environment For Journalists

· Ask security agents to find missing Vanguard journalist As...

EXCLUSIVE: Buhari orders probe of Isa Funtua, AMCON over keystone and Etisalat

Following the controversy generated by the leading opposition party,...

6 Signs your boyfriend thinks you are ugly -Take note of No. 2

They say there are three kinds of people; the...

2023: South-East, Middle Belt Forum Endorses Peter Obi

The South-East and Middle Belt Forum has endorsed the...

SOKOTO – BUA Cement Trains 60 Youths on Heavy-Duty Machinery Operation

By Muhammad Ibrahim, Sokoto BUA Cement has launched a Host...

Xenophobia, ‘Nigerians-Must-Go’ protests and ECOWAS Protocols

By Patrick Wemambu When visitors to a country become more...

Floods Wreak Havoc in Plateau, Bauchi, Niger, as FG Raises Red Alert Across Nigeria

Severe floods triggered by heavy downpours on Sunday have...

Access Bank: A Hub For Africa’s Financial Superpower

In today’s ever-evolving financial landscape, few institutions can claim...

Scrabble Stars Battle for N10m at Gov. Diri Championship

By Amgbare Ekaunkumo, Yenagoa Top Scrabble players from across Nigeria...

Northern CAN Leaders Visit Benue, Reject ‘Herders-Farmers Clash’ Narrative

...Pledge sustained advocacy...“Your presence is Christ sitting with us”...

Expect More Development — Gov. Aliyu Assures Sokoto Residents

By Muhammad Ibrahim, Sokoto Governor Ahmed Aliyu of Sokoto State...

We Have Brought Inclusive Development to Plateau — Governor Mutfwang

By Israel Adamu, Jos The people of Plateau State made...
spot_img

Related Articles

Popular Categories

spot_imgspot_img