x

Kwalejin Kimiyya Da Fasaha Da Jami’ar Aliko Dangote Sun Kulla Yarjejeniyar Alakar Karatu.

JABIRU HASSAN, Daga Kano.

A Tamar Litinin din data gabata, watau 29 ga watan Yuli, shekara ta 2024 Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic tare da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote dake Garin Wudil suka rattaba hannu akan jarjejeniyar kulla alakar gabatar da karatun Postgraduate Diploma a bangarorin Kimiyya, Fasaha da Kuma Kere-kere.

A jawabin da ya gabatar a yayin rattaba hannun, Shugaban Jami’ar Fasaha ta Wudil, Farfesa Musa Tukur Yakasai Ya bayyana matukar Jin dadinsa ga wannan hobbasa da Kwaleji Kimiyya ta Kano ta bijiro da shi wajen ganin ta cimma mafarkin da ta dade tana yi.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka zata samar da matukar cigaba wajen bunkasa harkokin Kere-kere a fadin Jihar Kano dama Kasa baki daya.

Farfesa Yakasai Ya jaddada cewa a yanzu Jami’arsu ta sahalewa Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, wato Kano State Polytechnic ta fara gabatar da karatun Postgraduate Diploma a fannoni guda 9, tare da tabbatar da cewa nan gaba kadan za’a Kara shigo da wasu sababbin kwasa-kwasan a wannan hadaka.

Ya kuma yabawa Shugaban Kwalejin, Dr. Abubakar Umar Farouq, FCA wajen jajircewarsa don ganin an cimma wannan nasara.

A nasa jawabin, Shugaban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, Dr. Abubakar Umar Farouq Ya bayyana matukar Jin dadinsa tare da mika godiya ga Allah da Ya nuna masa wannan rana ta saka hannun akan wannan yarjejeniya.

Ya Kara da cewa, wannan hadaka tsakanin makarantun Kimiyya da Fasaha mallakin Jihar Kano guda biyu zai matukar taimakawa kokarin da Gwamnatin Jihar Kano, karkashin Jagoranci Alhaji Abba Kabir Yusuf take wajen ganin ta bunkasa ilimi, musammam na bangaren Kimiyya da Fasaha.

Dr. Farouq Ya jaddada cewa wannan hadaka zata baiwa dumbin matasa da masu sha’awar cigaba da karatu damar cimma burikansu ba tare da wahala ba.

A karshe Ya godewa Shugaban Jami’ar ta Wudil gami da masu taimaka masa wajen ganin an cimma wannan nasara, tare da tabbatar da cewa Kwalejin Fasaha ta Kano za tayi duk Maiyiwuwa wajen ganin komai Ya tafi akan tsari.

Hot this week

IGP Restructures Police Monitoring Unit, Appoints DCP Aliyu Abubakar as Head

The Inspector-General of Police has approved the restructuring of...

Malami: Judge Threatens Contempt, Warns Counsel Against Unruly Conduct

By Francis WilfredJustice of the Federal High Court, Maitama,...

Court Jails Man Five Years for Recruiting Boys into Yahoo School

By Francis WilfredThe Benin Zonal Directorate of the has...

Neglect of Teachers Undermining Nigeria’s Education Quality, Demand Urgent Reforms

By Joyce Remi-BabayejuTeachers in the education sector have begun...

President Federation Cup: EFCC FC Beats Fire Service FC 1–0

By Francis WilfredThe football team of the secured a...

Zawan Group Calls for Fair Political Zoning in Jos South Ahead of 2027 Elections

By Israel Adamu, JosA socio-political group, Zawan Vanguard, has...

Akpoti-Uduaghan to Appeal N1bn Judgment, Alleges Misrepresentation of Evidence

A Senator representing Kogi Central, Natasha Akpoti-Uduaghan, has directed...

Bingham University to Award ₦231.3m Scholarships to 779 Students

By Israel Adamu, JosBingham University, Karu, Nasarawa State, says...

Kaduna Retirees Decry Unpaid ₦1bn Pension Arrears, Urge Governor Sani to Act on Agreement

By Achadu Gabriel, KadunaRetired Heads of Service and Permanent...

Kogi Reports Drop in Malaria Cases, Pledges Elimination Efforts

From Noah Ocheni, LokojaThe Kogi State Government says it...

Abuja Residents Applaud Tinubu, Wike Over Satellite Town Roads

By Joyce Remi-BabayejuResidents of satellite communities in Abuja, particularly...

Kogi Governor Ododo Pledges Youth Job Creation, NYSC Camp Upgrade

From Noah Ocheni, LokojaKogi State Governor Ahmed Usman Ododo...

ECWA Urges Members to Participate in 2027 Elections, Raises Concerns Over Insecurity and Roads

By Israel Adamu, JosThe Evangelical Church Winning All (ECWA)...

Related Articles

Popular Categories

spot_imgspot_img