x

Kantoman Goronyo Tare Hadin Gwiwar Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Mafakar “Yan Ta’adda

Must read

By Muhammad Ibrahim,Sokoto

A Kokarin Kantoman mulki na Goronyo Alh Kabiru S/ Fulani da dan Majalisar Jaha Mai Wakiltar Goronyo Nasiru Adamu na kawar da ta’addanci a Karamar Hukumar Mulki ta Goronyo.

Sun Jagoranci Jami’an Tsaro domin tarwatsa mafakar Yan Ta’adda a dazukan Giyawa ta Karamar Hukumar Mulkin Goronyo.

Tawagar Jami’an Tsaro wadda Kantoman Goronyo da Dan Majalisar Jaha Mai Wakiltar Goronyo suka Jagoranta sunkai samame a maboyar Yan Bindiga dake cikin dajin Giyawa.

Wannan yunkuri na cikin jajircewar Kantoman Goronyo da dan Majalisar Jaha mai wakiltar Goronyo a bisa jajircewar su tareda baiwa Jami’an Tsaro cikakkiyar kulawa akan aikin su.

Sun jagoranci Jami’an Tsaro da Al’ummar gari an kutsa a dajin Giyawa inda aka samu nasarar tarwatsa mafakar Yan Ta’adda.

Copyright DAYBREAK NIGERIA.

All rights reserved. This material, and other digital content on this website, may not be reproduced, published, broadcast, rewritten or redistributed in whole or in part without prior express written permission from DAYBREAK NIGERIA.

More articles

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisement -

Latest article