x

Neman Gafara: Tsohon  Gwamna Bafarawa Ya Roki Sakkwatawa Su Yafe Laifin Dake Tsakaninsu

Must read

By Muhammad Ibrahim,Sokoto
A ranar jiya Laraba, Dattijo tsohon gwamnan Jahar Sokoto Alh. Attahiru Dalhatu Bafarawa (Garkuwan Sokoto) ya roki daukacin al’ummar Sokoto da birni da Karkara, yaro da kuma Babba dasu yafemasa kura-kurensa da laifin dake tsakaninsu lokacin da yake jagorancin kujerar Gwamna tsawon shekaru takwas.
A Jihar Sokoto Gwamnatin Bafarawa da aka yi tsawon shekaru takwas na daga cikin Muhimman gwamnatoci da aka yi wadanda Sokoto da Sakkwatawa sunka amfana kuma sunka ji dadinta. Tabbas babu abinda ke tsakanin Bafarawa da Sakkwatawa banda Alkhiri
Yadda Allah SWT, zai tsayar da Dattijo Bafarawa gobe kiyoma ya tambaisa hakkin sama da mutum Miliyan Guda lokacin mulkinsa shine abinda Bafarawa ke kallo a yanzu ya roki gafarar Sakkwatawa. tsakanin jin dadin al’umma, kwancinyar hankalinsu da tsare dukiyoyinsu da tabbatar da Walwalarsu na daga cikin hakkin kowanne shugaba kuma Allah zai tambaisa wannan.
Nan take wani bawan Allah mai suna Usama ya yafewa Bafarawa dangane da hangen nesansa.
“Al’ummar jihar Sokoto ku shaida ni Usama B Lawal Rabah na yafewa Baba Bafarawa (Garkuwan Sokoto) duk wani hakki dake tsakaninmu na kasancewarsa Gwamnan jiharmu tsawon shekaru takwas. Allah yafemana dukkanmu”.

Copyright DAYBREAK NIGERIA.

All rights reserved. This material, and other digital content on this website, may not be reproduced, published, broadcast, rewritten or redistributed in whole or in part without prior express written permission from DAYBREAK NIGERIA.

More articles

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisement -

Latest article